10 Satumba 2024 - 10:28
An Nemi A Gurfanar Da Wadanda Suka Aikata Laifukan Lalata Da Fursunonin Falasdinu

Bramila Batten, wakiliyar babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan cin zarafin mata a lokutan yaki da tashe-tashen hankula, ta bayyana damuwarta dangane da rahotannin baya-bayan nan da wannan kungiya ta fitar game da mummunar tabarbarewar yanayin fursunonin da ake tsare da su a gidajen yarin yahudawan sahyoniya.

Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul-Baiti As - ABNA - ya habarta maku bisa nakaltowa daga shafin sadarwa na Qudus cewa: Bramila Batten, ta kara da cewa: "Ya kamata a gudanar da bincike mai zaman kansa, cikakke, wanda babu son kai kuma mai inganci daga kungiyoyin da suka dace da kuma na musamman na Majalisar Dinkin Duniya game da wadannan laifuka, ta yadda za a gurfanar da duk masu aikata laifuka, ba tare da la'akari da matsayinsu da akidarsu ba".

"Wadannan rahotanni masu matukar tayar da hankali game da cin zarafin mata da sauran munanan dabi'u da cin mutunci, a wasu lokuta suna iya kaiwa ga azabtarwa ta hanyar saduwar maza da mata na Palasdinawa da kuma cin zarafi mai yawa na a yayin faden da kuma barazanar fyade da fyade na gungun mutane, da kuma bayyana tsiraici da tube tufafin da ake yi akan tilas na don bincike na dogon lokaci, duka da bugun wutar lantarki ga al’aura, da kuma daukar hoton wadanda ake tsare tsirara ko rabin tsirara a wurare masu ban tsoro.

"Irin wadannan ayyuka na nuna kyama ba wai kawai keta hakkin bil'adama ne da mutuncin bil'adama ba ne, har ma da raunana kokarin da ake yi na samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin".